A yau jumma'a Mikel Arteta ya tat'tauna da manema labarai akan wasu abubuwa da suka shafi kungiyar Arsenal.
Mikel Arteta ya amsa tambayoyi da dama a yayin hiran nasa. Sai dae abinda yafi jan hankalin mutane a hiran na Arteta shine irin amsar da ya bayar akan tambayar da akayi masa akan maganar siyo sabbin yan wasa a wannan wata na Janairu.
Ga abinda yayi magana akai....
Arteta akan Maitland-Niles:
"Ainsley ya zo wurina ya bayyana dalilan da ya sa ya yi tunanin abin da ya fi dacewa a gare shi da kuma aikinsa shi ne ya bar kungiyar Arsenal domin ya yi imanin yin wasa da aiki a karkashin Jose wata dama ce mai kyau a gare shi. Hakan yasa muka amince masa yatafi As Roma.
Mikel Arteta Game da alkalin wasan da ya busa wasan Arsenal da man City:
Ko kadan baiyi dai'dai ba kuma ya bata s sakamakon wasan sosai. A babban wasa irin wannan baikamata ya busa wasan haka ba.
Arteta akan matomakar tsakiyar (Midfield) na Arsenal bayan Maitland Niles ya tafi.
Muna da karancin yan wasan tsakiya sosai a halin yanzu. Za mu matsa don siyo wani dan wasan tsakiya. Saboda muna da karancin yan tsakiya (Midfield) sosai.
Arteta a kan siyan sabon dan wasan gaba:
Muna da yanayi na musamman akan wannan al'amari domin akwai 'yan wasanmu uku da akwai yan damuwa atare dasu, a halin yanzu dole ne mu kasance dasu a hakan. zuwa yanzu 'yan wasan da suke nan suna da himma sosae.
Ko me Arteta yake nufi da wadannan maganganu nasa?
Admin
Prince Tije