DAN WASAN ARSENAL NUNO TAVARES DA KE ZAMAN ARO A KUNGIYAR MARSEILLE ZAI IYA DAWOWA

[Dan wasan Arsenal Nuno Tavares da ke zaman aro a kungiyar Marseille

Nuno Tavares ya yi fama a kakar wasansa ta farko a gasar Premier tare da kungiyar Arsenal, Amma yanzu  yana zaman aro a Marseille a Ligue 1.

Dan wasan mai shekaru 22 ya isa arewacin Landan ne daga Benfica a bara kuma ya samu damammaki da dama a bangaren hagu saboda raunin da Kieran Tierney ya samu.

Dan wasan baya na kasar Portugal ya buga wasanni 22 a gasar Premier, kuma yayin da bai cika yin fice ba, acikin kungiyar

Da zuwan Oleksandr Zinchenko a Arsenal, Tavares ya koma aro zuwa kasar France kuma har yanzu yana da makoma a Emirates idan ya ci gaba da buga abunda yake yi a kungiyar ta Faransa.

Kwarewar sa na kai hari na ci gaba da haskakawa, inda ya zura kwallaye uku a wasanni bakwai kacal da ya buga a gasar Ligue 1 kuma kociyan nasa yana hasashen yiwuwar kai hari a sauran kakar wasa ta bana.

"Wani lokaci ma ba ya gane halayensa," in ji shugaban Marseille Igor Tudor. 'Yana da wuya a bi shi lokacin da ya hanzarta.

Ku tofa ra'ayin bakinku game da wannan labarin..

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post